Friday, 29 December 2017

MUHIMMANCIN SALLAR DARE(QIYAMUL-LAI)

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
Bayan mukaddimah.....
Yan uwa musulmi masu albarka yau khudbar mu zata yi magana ne game da #MUHIMMANCIN_SALLAR_DARE (kiyamul laili)
Yan uwa musulmi a makon da ya gabata munyi khuduba ne game da sallar nafila..
To yau in sha Allah Zamu yi magana ne game da Sallar Dare wato kiyamul laili.
Hakika Allah ya yabi masu yin sallar dare a cikin suratul sajadah, "ALLAH ya kan rokon sa kuma suna ciyar da abunda muka basu,  Suna tashi sallar dare,  suna da makoma ta kwarai"
Hakika saboda kaunar mu da Allah yake yi  ya bamu damar aikata ibadu kala kala har ma yakan bamu lada idan mun aikata.
Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Mafificiyar sallah itace sallar nafila bayan ta sai sallar dare"
Hakama Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana cewa "Sallar da Allah yafi so itace sallar dare"
Yan uwa musulmi masu albarka lallai wannan sallar wato sallar dare tana karawa ihlasi.
Hakika tsayuwa cikin dare yana karawa bawa tsoron Allah da natsuwa, Hakama duk ranar da dan Adam yayi sallah to zaiji natsuwa da kwanciyar hankali.
Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace ma sahabin sa "In fada maka wata hanyar alkhairi??
Sai sahabin yace eh, Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace 'Ka yawaita azumin nafila, Da sadaqah domin sadaqah tana cinye zunubai kamar yadda ruwa suke kashe wuta sai kuma ka lizimci sallar dare"
Yan uwa musulmi masu albarka muhimmancin sallar dare baya misaltuwa, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "ALLAH yayi rahama ga wanda ya tashi yayi sallar dare"
Hakika yan uwa musulmi sallar dare tana cikin salloli masu karawa dan Adam ihklas.
Manzo sallal lahu alaihi wassalam shine baban abun koyi garemu baki daya, Hakika Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya kasance yana tsayuwar dare har kafasun sa su fara tsagewa har Aisha radiyyallahu anha tace masa miyasa kana Manzo Allah kake Ibadah kamar haka??
Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace Shin bazan zamo bawa mai godiya ba??
Yan uwa musulmi masu albarka hakika yawan yin sallar dare yana kauda bala'oi da musibuh.
Sallar Dare tana gyara halaye kuma tana gyara halaye.
Ibn hajr asqalani yace 'Ita sallar dare tana wanke zukata'
Saboda muhimmancin sallar dare Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya hore mu da yin sallar dare inda yake cewa "NA hore Ku da sallar dare domin tana share zukata"
Hakika sallar dare tana kara lafiya da kwarin jiki,
Ina wadanda basu da lafiya likita yace sai sun rika motsa jiki duk safiya???
To ga exercise daga likitan likitoci Manzo sallal lahu alaihi wassalam idan har ka tsarkake niya to hakika Allah zai baka lafiya da yardar sa.
Ibn Salam ya ruwaito daga cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Ku yada sallama a tsakanin ku Ku raba Sadakar abinci Ku sada zumunta kuyi sallar dare"
Duk mai kokarin sallar dare Allah zai haska zuciyar sa....
Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana baiwa sahabbai labari cewa "A cikin aljannah akwai wasu benaye masu tsawo ana ganin abunda ke ciki saboda tsabar hasken su a wata ruwayar har matan da suke ciki ya kwatanta, Sai wani mutanen karkara yace ya Manzo Allah wake da wadannan benayen??
Sai Manzo Allah yace na wadanda suka iya magana ne (Magana mai kyau Sadaka ce) da wanda ya sada zumunci da wanda ya yawaita azumi da wanda ya lizimci sallar dare "
ALLAH Ya umarci Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya tashi yayi sallar dare" KA TASHI KAYI SALLAR DARE KA ROKI UBANGIJIN KA "
Manzo sallal lahu lahu alaihi yayi addu'a ga wanda ya tada iyalinsa suka yi sallar dare.
Idan mata ta tashi zatayi to tana iya tada mijinta Shima idan bai tashi ba tana iya yayyafa masa ruwa amma idan babu matsala 
Yan uwa musulmi masu albarka saboda muhimmancin sallar dare Umar bn Khaddab ya kasance yana tada iyalinsa suyi sallah a karshen dare.
Hakika ALLAH yana sauka a sulisin dare a saman duniyar nan yana cewa "INA MASU NEMAN GAFARA INYI MASU INA MASU NEMAN BIYAN BUKATA IN BIYA MASHI??"
Yan uwa musulmi a yanzu mun bar sallar dare sai a lokachin azumin ramadana.
Idan baka iya tashi da dare to kana iya yin sallar ka bayan isha'i.
Yan uwa musulmi lokachin da yakamata muyi sallar shine misalin karfe 2,3,4 domin shine sulisin dare.
A yanzu muna ganin yadda a duniyance kowa yana neman hanyar rayuwa, Kama daga bidar kudi da sauran su.
Ita lahira babu batun kudi ko wani abu hakika yakamata mu maida hankali dan lahirar mu.
Lallai kada mu kuskura shaidan yayi tasiri garemu.
Mai hankali ne wanda keyi lahirar sa tanadi kafin yaje.
ALLAH Ka taimakemu da taimakon ka ya ubangiji ka yafe mana kurakuren mu.
Ya Allah ka biya mana bukatun mu kayi rahama ga mamatan mu ya amintar damu daga abunda muke tsoro.
(Dan Adam ajizi ne Allah ka gafarta mana abunda muka yi kuskure)
©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 10-Rabi'ul akheer-1439
29 Friday -December-2017 AB

Friday, 15 December 2017

MUHIMMANCIN NAFILAH

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH   DAGA MASJID ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon  limam Sani Abi hurairah Tsafe ya gabatar da khudbar ne akan #MUHIMMANCIN_NAFILAH

Bayan mukaddimah......

Yan uwa musulmi masu albarka hakika gaskiyar zance shine Alqur'ani Mai tsarki, Mafi kyawun shiriya itace shiriya ta Annabi Muhammadu sallal lahu alaihi wassalam, Mafi sharrin ayyuka shine kirkirar abu ga addini.

Yan uwa musulmi masu albarka ina maku Nasiha tare da ni kaina da muji tsoron ALLAH domin jin tsoron ALLAH shine jagora ga rayuwar mu, ALLAH yana fada cikin suratul kasas cewa "WANNAN GIDAN NA LAHIRA MU SANYA SHINE GA MASU TSORON ALLAH HAKIKA AQIBA MAI KYAU ITA KUWA AQIBA MAI KYAU TANA GA MASU TSORON ALLAH"

Saboda kaunar da ALLAH keyi mana ya sanya mana abubuwa da Zamu amfana dasu, kamar nafilfili da sauransu,  Nafila ta sallah tana Matukar muhimmancin ga ibada,

Yan uwa musulmi masu albarka sallah itace abunda za'a fara bincike a gobe Kiyama, Manzo sallal lahu alaihi wassalam na cewa "Farkon abunda za'a yiwa dan Adam hisabi akanshi shine sallah idan tayi kyau to dan Adam ya dace idan kuma an samu matsala sai ALLAH ya umarci mala'iku su binciki shin akwai nafila?
Idan akwai to sai ayi amfani da ita wajen cike sallar farilla"

Haka ma a azumi da zakkah sai a diba idan akwai wakafi da sauran ibadu!!

Kenan koda a wannan hadisin muka tsaya lallai zamu fahimci cewa nafila nada matukar muhimmanci.

A wajen yin ibadar sallah ana bukatar natsuwa sosai Ibn Abbas ya ruwaito yace" Sai kana da natsuwa sannan sallahr ka zata karbu "

Yan uwa musulmi masu albarka yawan yin nafila yana sa mutun yazama abokin Manzo sallal lahu alaihi wassalam a gidan aljannah 😁

Akwai wani sahabin Manzo sallal Sallal lahu alaihi wassalam idan Annabi zai yi alwala sai sahabin ya dauki talkaman Annabi ya rike a hannunsa hakama idan Manzo sallal lahu alaihi wassalam zai yi sallah yakan tsaya har sai Annabi ya fito, Wata rana sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya tambaye shi mi kake bukata inyi maka??

Sai yace ina so in zama abokin ka a gidan aljannah.....

Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace to ka taimake ni da yin nafila a koda yaushe. "

Yan uwa musulmi masu albarka yawaita nafila na kara kusan tar da dan Adam ga ubangiji, ALLAH madaukakin sarki na cewa" BAWA BAZAI GUSHE YANA SUJJADAH HAR SAI NA SOSHI "

Yan uwa musulmi masu albarka yawaita yin nafila kara maka kusanci da ubangiji ALLAH

Abdullahi bn Umar ya ruwaito cewa" Kafin sallar azahar kayi raka'a 2 bayan sallar kuma kayi 2 la'asar kayi 2 bayan ta kayi 2 hakama a magrib da isha'i hakama a sallar asuba kafin ta wato sallar fajir "

Haka ma Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Duk wanda yake yawaita yin nafila raka'a 12 a rana ALLAH zai gina mashi gida a aljannah "

Haka ma Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana cewa" Kuyi raka'a 2 kafin magrib ya fadi haka har sau uku amma ga wanda yake sa hali "

Haka ma Aisha radiyyallahu anha ta ruwaito cewa" Manzo sallal lahu alaihi wassalam bai taba barin nafila ba a lokachin sallar asuba ba "

Yan uwa musulmi masu albarka hadisin dake magana game da ba'a sallah bayan la'asar na nufin idan an dade da gama sallar ne.

Daga cikin nafilolin da ake bukatar yawaita aikatawa akwai sallar duha wato ita anayi ta ne da safe, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Dan Adam yana da gabobi guda 360 ana bukatar a kullum kabada Sadaka kwatan kwacin haka sai sahabbai suka ce to idan baka da kudin bada Sadakar??  Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace to ka tsaftace massallaci (kamar shara ko kuma dauke wani tsinke) koda ma ace ka gaza haka to kayi sallar duha "

Yan uwa musulmi masu albarka hakika addinin musulunci yana da Matukar dadi da kuma garabasa ga wani hadisi daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam cewa

" Duk wanda ya fito daga gida yayi aikatawa zaije massallaci to ana rubuta mashi ladar aikin hajji da umrah "

Hakika yan uwa musulmi idan muka yawaita yin nafila za'a rubuta sunayen mu cikin illiyun 😁😁

Yan uwa musulmi bayan sallar asuba yana da kyau mu rika zaunawa koda awa guda ko biyu ne Muna yin tasbih domin falalar dake ciki, Hadisi daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam na cewa "Bayan kammala sallar asuba ka zauna har rana ta fito kana da ladar aikin hajji cikakke cikakke cikakke!!

Yan uwa musulmi dole ne mu rage yawan zama ana hira ana surutu fiye da awa guda alhali zaman baida wani amfani garemu,

Imam Muslim ya ruwaito daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam cewa "Dayanku bazai yi alwala yana jiran sallah ba face wuta ta haramta gareshi!!"

Yan uwa musulmi kunji falala mai kyau kenan masu zuwa massallaci da Wuri suna jiran limam sun samu shiga a wannan.

Sannan kuma yan uwa musulmi yana da kyau mu yawaita yin nafila a gidajen mu domin Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada mu maida gidajen mu kamar makabartu (Domin ba'a sallah a makabarta)

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Mafificin nafila itace nafillar da akayi a gida "

Yan uwa musulmi kada mu rangwantar da kawunan mu mu kashe jikin mu da hira da surutai marar sa amfani domin wallahi akwai ranar da Zamu nemi ina ma ace Zamu yi aiki koda na kwayar zarra ne!! 😷😷

Akwai falala mai yawa a cikin sallar nafila, Manzo sallal lahu alaihi wassalam "SALLAR fajir (Kafin asuba) tafi duniya da abunda ke cikin ta"


To yan uwa musulmi kunji fa......

Tabi'ai da sahabbai sun kasance idan wani yayi laifi yana zuwa yayi nafila ya roki Allah ya gafarta masa.

*Sallar nafila tana daga Darajar dan Adam a wurin ALLAH

Hakika sahabbai da Tabi'ai suna yawaita yin nafila domin tsannanin koyi da Annabi, Saboda Annabi ya karantar dasu kuma yayi a gaban su har ma ya kwadaitar da wannan ibadar.

Yawaita nafila yana kawo abubuwa kamar haka :

*Gidan mutun yana albarka

*Darajar dan Adam tana karuwa

*Yana sanya mutun yazama abokin Manzo sallal lahu alaihi wassalam a gidan aljannah.

*Nafila na zama abokiyar hira ga dan Adam a cikin kabari.

*Zai kara maka son ALLAH

*Tana maida dan Adam yazama mutanen kirki.

*Samun ladar aikin hajji da umrah

*Kankarewar Zunubai.!!

Yan uwa musulmi masu albarka a yadda duniya ta chanza a yanzu dole ne mu rungumi koyar wa Manzo sallal lahu alaihi wassalam da duk abubuwan da ya karantar damu.

ALLAH ka gafarta mana kayi mana rahama kabamu lafiya da zaman lafiya, Ya ubangiji ALLAH kayi rahama garemu ka biya mana bukatun mu ka haskaka rayuwar mu, Ameen

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 20-Rabi'ul auwal-1439
Friday 15-December-2017 AB

Saturday, 15 July 2017

MEYASA BA'A KARBA ADDU'OINMU?

🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅
*MEYASA MUKE ADDU'AH, AMMA SAI MUGA KAMAR BA'A KARBA MANA???*
🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆

```An tambayu Ibrahim bn Adham(RH) akan cewa meya samemu ne, muna Addu'ah amma ba'a karba mana??

Sai yace: Zukatanku sun mutu da Abubuwa takwas(8).

NA FARKO; Munsan Allah, amma ba muyi mashi biyayya(ma'ana; munsan hakkin Allah, amma bamu gabatar mashi da hakkinshi).

NA BIYU; Muna karanta Alkur'ani, amma bamu aiki dashi(ma'ana: Bamu aiki da iyakokin da Allah ya gindaya a cikin Qur'anin).

NA UKU: Munce munason Manzon Allah (Salallahu alaihi wasallam), amma sai muka yi mashi tawaye, muka kiyin amfani da sunnar shi.

NA HUDU: Munsan cewa Shaidan makiyinmu ne, amma sai muka sakar mashi akala muna binshi.(Muna yi mashi biyayya wajen sabon Allah).

NA BIYAR: Munsan cewa Aljanna gaskiya ce, amma bamu aiki domin mu shigeta.

NA SHIDA: Munsan cewa wuta gaskiya ce, amma bamu guje mata.

NA BAKWAI: Mun wayi gari mun shagaltu da aiboban(harkokin) mutane, mu kuma mun bar namu aiboban(harkokin).

NA TAKWAS: Kun binne mataccinku, amma Baku lura da kuma wataran za'a binneku.

NA TARA: Mun ce, muna tsoron mutuwa, amma ba muyi mata tanadi ba.

NA GOMA: Muna cinye ni'imomin Allah, Amma bamu gode mashi(muna cinye abincin Allah, abin shan Allah, da sauran ni'imomi amma mun kasa gode mashi).

Wadannan da wasunsu sune dalillan dake sa muke rokon Allah sai Allah ya kyalemu da dabararmu.

Yaa Allah ka bamu ikon gode maka.
Yaa Allah ka karo mana ni'imominka ta hanyar da muka sani da wacce bamu sani ba.```

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
+2348064734911
+2349030201868

SHAFUKAN SADA ZUMUNTA DOMIN BIBIYARMU.

atstsamawy@gmail.com

hashimusurajo5@gmail.com

I G @ abbansinan

http://hashimtsamiya.blogspot.com/

http://abbansinaan.blogspot.com/

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com/

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com/

https://mobile.facebook/hashimusurajo.tsamiya/

Saturday, 1 July 2017

GORON SALLAH

*MUHADARA MAI TAKEN; AMFANI DA KUMA ILLOLIN SOCIAL MEDIA*

   Muhadara mai taken amfani da kuma illolin social media a cikin al'umma wacce kwamitin matasa na *SHABABU AHLISSUNNAH WALJAMA'AH SUKA SHIRYA DOMIN GORON SALLAH,* muhadarar wacce *USTAZ MUSA S LAWAL(Abu salih Ibn salih)* ya gabatar a masallacin *UTHMAN BIN AFFAN TSAFE,*

Wallahi akwai abubuwan da ya kamata mu amfana dasu kwarai da gaske a cikin wannan muhadara.
Kai dai kawai shiga link dake kasa domin saukewa a wayanka.
👇👇👇👇👇👇👇👇
*Amfani da illolin social media by Ustaz musa s lawal Tsafe*

http://darulfikr.com/s/24715

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi akan wannan lecture da yayi mana.

darulfikr.com takuce domin yada Sunnah a koda yaushe.

Copyright©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya
+2348064734911
+2349030201868

Monday, 26 June 2017

2017 RAMADAN TAFSEER

*2017 COMPLETE  RAMADAN  TAFSEER*

   COMPLETE  2017 RAMADAN  TAFSEER DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABU HURAIRA AREA  II TSAFE.

  wanda Malam Sani Liman Tsafe (ABI HURAIRA)   yake gabatarwa a Area II Tsafe, jahar Zamfara  Nigeria.

Shiga  links dake kasa  Domin saukewa Cikin sauki ka saurara  Cikin kyakykyawan Sauti.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

01 Ramadan Tafseer 1438Ah Suratul Nisa i By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24378

02 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24379

03 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24380

04 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24381

05 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Sani LimanTsafe
http://darulfikr.com/s/24382

08 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24383

09 Ramadan Tafseer Akan Hukunce Hukunce Mata Na Dare By Mal San Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24384

10 Ramadan Tafseer Na Dare By Abu-Hurairah Tsafe
http://darulfikr.com/s/24385

11 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24386

12 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24387

14 Ramadan Tafseer 1438 Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24388

15 Ramadan Tafseer Na Dare Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24389

16 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal SaniLiman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24390

17 Ramadan Tafseer Na Dare 1438 By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24391

19 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24392

20 Ramadan Tafseer 1438 Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24393

21 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24394

Kasance do darulfikr.com a koda yaushe domin  samun karatuttukan maluman  sunnah.

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

2017 RAMADAN TAFSEER

*2017 COMPLETE  RAMADAN  TAFSEER*

   COMPLETE  2017 RAMADAN  TAFSEER DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABU HURAIRA AREA  II TSAFE.

  wanda Malam Sani Liman Tsafe (ABI HURAIRA)   yake gabatarwa a Area II Tsafe, haha Zamfara  Nigeria.

Shiga  links dake kasa  Domin saukewa Cikin saki LA saurara  Cikin kyakykyawan Saudi.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

01 Ramadan Tafseer 1438Ah Suratul Nisa i By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24378

02 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24379

03 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24380

04 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24381

05 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Sani LimanTsafe
http://darulfikr.com/s/24382

08 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24383

09 Ramadan Tafseer Akan Hukunce Hukunce Mata Na Dare By Mal San Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24384

10 Ramadan Tafseer Na Dare By Abu-Hurairah Tsafe
http://darulfikr.com/s/24385

11 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24386

12 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24387

14 Ramadan Tafseer 1438 Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24388

15 Ramadan Tafseer Na Dare Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24389

16 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal SaniLiman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24390

17 Ramadan Tafseer Na Dare 1438 By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24391

19 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24392

20 Ramadan Tafseer 1438 Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24393

21 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24394

Kasance do darulfikr.com a koda yaushe domin  samun karatuttukan maluman  sunnah.

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

IN ANSHA RUWA A KOMA AIKI

IN ANSHA RUWA....

*IN ANSHA RUWA A KOMA AIKI!!!*
NASIHA KAFIN ZUWAN LIMAN DAGA MASALLACIN IDI NA DAYA DAKE GARIN TSAFE, WACCE USTAZ MUSA S LAWAL YA GABATAR MAI TAKEN: _MUHIMMANCIN LOKACI, BAYAN RAMADANA SAI ME?_   DAN UWA YA KAMATA KA SAUKE DOMIN AKWAI ABUBUWAN DA YA KAMATA KASANI KWARAI DA GASKE, MALAM YA BADA ILIMI.
Muhimmancin lokaci meya kamata in aikata bayan ramadan?
DAGA BAKIN *_USTAZ MUSA S LAWAL TSAFE(ABU SALIH IBN SALIH)_*
http://darulfikr.com/s/24540
Kasance da darulfikr.com a koda yaushe domin samun karatukan maluman Sunnah a saukake.
Darulfikr.com takuce domin yada Sunnah.
Copyright©
*_Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)_*
+2348064734911
+2349030201868

Monday, 22 May 2017

AZUMIN WATAN RAMADHANA

🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉
*AZUMIN WATAN RAMADANA*
🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇

*بسم الله الرحمن الرحيم*

_Rubutawa;_ *HASHIM SURAJO UBA(ABU SINÃN)*

```ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU.

  Godiya ta tabbata ga Allah s.w.t shi kadai Wanda yayi mana umurni da azumtar ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada, Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da ibadar azumi da sauran ibadoji.

Bayan haka;

FALALAR WATAN RAMADANA DA AZUMI A CIKIN WATAN.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan ramadana ya shigo, ana bude kofofin sama, ana kulle kofofin jahannama, ana daure shaidanu.
A wani hadisin kuwa manzon Allah s.a.w cewa yayi" Dukkan wani aiki da dan Adam zaiyi, ana lunka aikin da lada goma irinsa, idan a ramadana ne, ana lunkashi zuwa lunki (700), sai Allah mai girma da daukaka yace ;  banda azumi, domin azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa Wanda yayi shi, yabar matarshi da abubuwan da yakeso, da abinci, da abin sha saboda ni, mai azumi Nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki (shan ruwa) da farin ciki lokacin haduwarshi da Allah, yamin/warin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

ABUBUWAN DA SUKA WAJABA GAREKA A RAMADANA

Ya dan uwa

Kasani cewa Allah ya wajabta mana azumi domin mu bauta masa dashi, sannan kuma ya kasance cewa azuminka ya zamto karbabbe mai amfani.
Dole ne ka kiyaye wadannan abubuwan da zasu zo domin samun cikakkar lada;

1- kiyaye sallah; Da yawa daga cikin masu azumi suna wasa da sallah, bayan kuwa cewa tana daga cikin gimshikan addini, barinta kuma yana kai mutum ga kafurci.

2- Dole ka kasance mai kyawawan dabi'u; Dole ne mu tsoraci kafurci da zagin addini, da aikata muna nan dabi'u a cikin mutane, kafirci yana fitar da musulmi daga addini.

3- Dole ne mu kiyaye halshenmu da sukar juna.
 
Manzon Allah s.a.w yana cewa; "idan dayanku yana azumi, to kada ya fadi maganganun da basu dace ba, idan wani ya zageka ko ya nemi yayi fada da kai, sai kace mashi ni azumi Nike, ni azumi Nike.

4- Ka nisanci zuwa wurin da ake aikata barna! Ko kallon fina-finai na banza, domin hakan zai kai ga bata azuminka.

5- Ka yawaita sadaka ga makusantanka da mabukata, da ziyartar yan uwanka.

6- Ka yawaita zikiri da karatun Qur'ani da saurararshi, da bibiyar ma'anoninsa, da aiki da karantar warshi, sannan da zuwa masallatai domin daukar darussa masu amfani, kamar sauraran tafsirai, yin i'itikafi a masallaci idan goman karshe na ramadana suka kama.

7- karanta takardu akan azumi, domin sanin hukunce- hukuncen da suka shafi azumi, ta yarda zakasan cewa cin abinci ko abin sha da mantuwa baya karya azumi, kasan cewa ita janaba wacce ta sameka da daddare bata hana ka daukar azumi da sauransu.

LADUBBAN DA SUKA SHAFI AZUMI.

1- kiyaye halshe; Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda bai bar zancen karya ba, da aiki da zancen karya, Allah baya da bukatar barin cinsa ko shansa.

2- BUDA BAKI DA SAHUR DA ADDU'AH.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan dayanku zaiyi buda baki, to ya fara da dabino domin akwai albarka a ciki, idan bai samu dabino ba toh sai yayi da ruwa, domin suna tsalkakewa.
Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi buda baki yana fadar;
ذهب الظمأ، وابتلت العروق، وثبت الأجر، إن شاء الله.

Ma'ana: "YUNWA TA TAFI, GABOBI SUN DAI DAI TA, LADA TA TABBATA DA YARDAR ALLAH".
Manzon Allah s.a.w yace; "mutane baza su gushe suna samun alkhairi ba matukar suna gaggauta buda baki.

Anan dole mu gujewa muna nan akeedun shi'ah wadanda basa shan ruwa sai duhu ya shigo sosai, suna kafa hujja da ayar Qur'ani dake cikin suratul bakara, inda Allah s.w.t yake cewa; "...sannan Ku cika azumi zuwa dare. Wanman magana malamai sunyi bayanin me ake nufi tun da dadewa, mai Neman Karin bayani ya duba tafsirin "Aisarat-tafaseer, na jabir jaza'iry."

Manzon Allah s.a.w yace"kuyi sahur, domin a cikin yin sahur akwai albarka."

Manzon Allah s.a.w yace"Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da an rage komai daga ciki ba.

3-  DAGA CIKIN FA'IDOJIN AZUMI

   Duk Wanda yayi azumin ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbansa.

Duk Wanda yayi tsayuwar ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.(ma'ana: tsayuwar tarawihi da kiyamul-laili.)

4- WADANDA AKA YIWA RANGWAMEN AZUMI.

   *Marar lafiya da matafiyi, zasu ranka saboda fadar Allah s.w.t cewa;"Wanda ya kasance a cikinku marar lafiya ko akan hanyar tafiya, zai ranka azumin a kwanakin sauran watanni."
Amma marar lafiya Wanda ba'asa ran warkewa a kusa, toh sai ya rinka ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mai haila, da jinin haihuwa zasu aje azumi, saboda fadar ummuna Aisha R.A; "mun kasance ana umurtanmu da ranka azumi, amma ba'a umurtanmu da ranka sallah.[Bukhari da Muslim].

* Dattijo da dattijiya, wadanda sun tsufa sosai basa iya daukar azumi toh zasu ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mace mai ciki da mai shayarwa idan sunji tsoron rayukansu, toh zasu aje azumi sannan su ranka kawai, amma idan suna jin tsoron yayansu ne kawai, toh zasu ranka kuma su ciyar.

5- ABUBUWAN DAKE BATA AZUMI.

Abubuwan dake bata azumi sun kasu gida biyu:
Na farko; Abunda ke bata azumi Wanda ke wajabta rankawa kawai;

* Cin abinci ko abinsha da gangan.

* Yin amai da gan gan, saboda fadar annabi Muhammad s.a.w cewa: " Duk Wanda yayi amai, toh zai ranka azumi.[Hakim ya ruwaito]

* Mace mai haila da mai haihuwa, koda sauran mintuna kadan ayi buda baki tazo musu, toh zasu ranka azumin.

* Istimna'i(masturbation) wasa da al'aura da hannunka har maniyyi ya fito shima yana bata azumi kuma sai ka ranka.

Abu na biyu dake bata azumi kuma yake wajabta ranko da kaffara shine JIMA'I, akan maganar malamai kaffarar shine yanta baiwa ko azumin kwana sittin(60) a Jere.

6- ABUBUWAN DA BASU BATA AZUMI

* Cin abinci ko abinsha da mantuwa, ko da kuskure ko da tilasci! Babu ranko kuma babu kaffara, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa"Wanda ya manta yana azumi ya ci ko ya sha toh ya cika azuminsa, Allah ne ya ciyar dashi kuma ya shayar dashi.[Bukhari da Muslim]

* Amai ba dagan gan ba.

* Yin aswaki a kowane lokaci ko brush da sauransu.

* Dandana abinci da sharadin kada ka bari ya wuce maka.

* Sumbantar matarka, da sharadin kada akai ga aikata jima'i. Saboda manzon Allah s.a.w ya kasance yana sumbantar Aisha alhali yana azumi[Bukhari da Muslim].

* Cirewar hakori, ko zubar jini daga baki ko hanci.

* idan Alfijir ya keto alhali abunsha na hannunka, kada ka aje har sai ka biya bukatarka.

*jinkirta wankan janaba ko haila ko na haihuwa daga dare zuwa hudowar alfijir. Abunda yafi shine ayi gaugawar yi kafin sallar asuba.

Muna rokon Allah ya amfanar damu da abunda muka rubuta, Allah yasa munyi domin Neman yardar shi, Allah ya sanya ibadojin da zamu gabatar a ramadana su zamo karbabbu, kuma su zamo sanadiyyar tsira garemu duniya da lahira. Inda mukayi kuskure Allah ya shefeshi daga idanun masu karatu ya fahimtar dasu tare damu gabaki daya. Allah ya doramu akan tafarki madaidaici.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.

COPYRIGHT©
Hashim Surajo Uba(ABU SINÃN)```

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.wordpress.com

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

+2348064734911
+2348064734911

DABI'UN MAGABATA A CIKIN WATAN RAMADHANA

🍌🍌🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍌🍌
*DABI'UN MAGABATA A CIKIN WATAN RAMADANA*
🍇🍇🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍇🍇

_Rubutawa;_ *Hashim Ibn Surajo Ibn Uba(ABU SINÃN)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

```Assalamu Alaikum warahmatullahi wabarakatuhu.

Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda yayi umurni da azumtar watan ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w, Wanda ya koya mana yanda zamu gabatar da azumin.

Bayan haka;

Magabata suna da wasu dabi'u da ayuka da zantuka a cikin ramadana, watan ramadana shine watan da Allah s.w.t ke cewa; "watan ramadana Wanda q cikinshi ne aka saukar da Qurani, domin shiriya ga mutane, da kuma bayanai game da shiriyar....[bakara 185]

Magabata na kwarai suna da ayukan da suke aikatawa a ramadana  fiye da sauran watanni.  Daga cikin magabatan akwai;
*IMAMU MALIK IBN ANAS(imamu darul hijra) ya kasance baya dakatar da karatuka a masallacin Annabi Muhammad s.a.w sai a ramadana, domin yana shagaltuwa da karatun Qurani ne kawai.

*SUFYANUS-THAURY R.H; ya kasance idan Ramadana ya shigo, yana barin dukkan wasu ibadodi, yana shagaltuwa da tilawar Qur'ani.

* MUHAMMAD IBN ISMA'IL AL-BUKHARI(mai sahihul-bukhari): ya kasance a cikin duk yini daya yana sauke Qur'ani, yana tsayuwar tarawihi acikin kwana uku na tqrawihin yana sauke Quran.

*SA'ID IBN JUBAIR: ya kasance yana saukar Qur'an a duk kwana biyu.

* ABU AWANAH yace; naga IMAMU QATADA yana karantar da Qur'an a watan ramadana.

*IMAMU QATADA; ya kasance yana saukar Qur'ani a duk bayan kwana bakwai, idan ramadana ya shigo yana sauka duk kwana uku, idan kwanaki goma na karshe suka shigo yana saukewa a kowane dare.

*RABEEY IBN SULAIMAN(Dalibin imamush-shafi'i) R.H yana cewa; imamush-shafi'i ya kasance yana saukar Qur'ani a ramadana sau sittin (60)[kowace rana sau biyu] a kowane wata yana sauka sau talatin(30) bayan ramadana.

    Kiyamul-laili aikin Annabi Muhammad s.a.w da sahabbansa ne, Aisha R.A take cewa; "kada kubar tsayuwar dare, domin Manzon Allah s.a.w bai taba barinta ba, idan baya lafiya yana yi a zaune.

* Umar Ibn khaddab R.A ya kasance yana sallar dare dai dai gwargwado, idan dare ya raba, said ya tayar da iyalansa domin yin sallar, yana cewa SALLAH! SALLAH!! SALLAH!!! Sannan sai ya karanto aya ta 132 dake cikin suratu Daha, inda Allah madaukakin sarki yake cewa; "Ka umurci iyalanka da yin SALLAH ka kwadaitar dasu akanta, bamu tambayarka wani arziki mine masu azurtaka....

  Wannan shine dabi'un magabata na kwarai a watan ramadana, to mu ya halinmu yake a wannan wata mai albarka???

* Abdullahi Ibn umar(Allah ya kara masu yarda) ya kasance yana yin azumi ba ya buda baki(shan ruwa) sai tare da talakawa, ya kasance idan yana cin abinci sai wani mabukaci yazo ya tambaya sai ya tashi daga abincin ya mika masa, ya wuce da azumi ba tare da yayi sahur ba.

  Wadannan sune magabata na kwarai, kuzo Mani da irinsu a wannan zamanin yã Ku masu da'awar salafiyya da Sunnah!?

*YUNUS IBN YAZEED yake cewa; IBN SHIHAB AZ-ZUHURY ya kasance idan ramadana ya shigo yana cewa; "Wannan watan Qur'ani ne, da kuma ciyar da abinci".

* HAMMAD IBN ABI SULAIMAN ya kasance yana ciyar da mutum dari biyar(500) a watan ramadana. Ya kasance kuma yana ba kowane dayansu dirhami Dari(100).

  Yã yan uwa na masu daraja ya kamata mu kwatanta rabin abunda magabatanmu na kwarai suka aikata na ayukan alkhairi, kada mu shagaltu da abunda bazai amfanemu ba, daga baya mu koma da na sani! Allah madaukakin sarki yana cewa;"ومن أعرض عن ذكري فإن له معيشة ضنكا ونحشره يوم القيامة أعمى، قال رب لم حشرتني أعمى وقد كنت بصيرا، قال كذلك أتتك آياتنا فنسيتها وكذلك اليوم تنسى، وكذلك نجزي من أسرف ولم يؤمن بآيات ربه، ولعذاب الآخرة أشد وأبقى.

Allah yq karemu.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.



COPYRIGHT©
Hashim Ibn Surajo Ibn Uba(ABU SINÃN)```

atstsamawy@gmail.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.WordPress.com

http://shababusunnahtsafe.mywapblog.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

+2348064734911
+2349030201868

YA YA ZAMU FUSKANCI RAMADANA???

🍌🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍌
*YA YA ZAMU FUSKANCI RAMADANA???*
🍇🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍇

_Rubutawa:_ *Hashim Ibn Siraj Ibn Uba{ABU SINÃN}*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda ya wajabta mana yin azumin watan ramadana, Tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada  Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da azumin ramadana.

Bayan haka;

Allah s.w.t yana fada a cikin suratul bakara aya ta 185 cewa;" watan ramadana Wanda a cikinsa ne aka saukar da Qur'ani domin shiriya ga mutane da kuma bayyanar da shiriyar....."

Ya yan uwa

Allah s.w.t ya kebance watan ramadana da kebantattun abubuwa masu yawa akan waninsa. Daga cikin abubuwan akwai;

* Fadar manzon Allah s.a.w cewa: warin bakin mai azumi, yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.
* Mala'iku na nemawa mai azumi gafara har zuwa lokacin da zaiyi buda baki.
* Ana tsare shaidanu a cikin Ramadana.
* Ana bude kofofin aljanna, ana rufe kofofin wuta.
* A cikin Ramadana ne Daren lailatul kadri yake, wadda tafi wata dubu Alkhairi.
* Allah na gafartawa mai azumi a karshen daren ramadana.

Ya yan uwa
Da wane irin abu zamu tarbi ramadana? Da wasannin banza??? Ko da zuwa kallon kwallo??? Ko da kallon fina finai???
Muna neman Allah ya tsaremu da aikata daya daga cikinsu a wannan wata mai albarka.

Shi bawan Allah na kwarai yana fuskantar ramadana da tuba zuwa ga Allah, yana mika lokuttanshi gaba daya domin yin ayukan kwarai, bawan Allah na kwarai shine mai rokon Allah akan ya karba masa ibadojinsa da addu'oinsa.

1- AZUMI

Manzon Allah s.a.w yana cewa; "Dukkan wani aiki da mutum zai yi, yana da ladar goma irinsa, amma ga azumi ana lunka aikin zuwa lunki dari bakwai(700). Allah mai girma da daukaka yace; banda azumi! Azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa masu azumi,(ma'ana babu Wanda yasan adadin ladar mai azumi sai Allah) sun bar abubuwan da suke sha'awa da kauna, sun bar abinci da abin sha saboda ni, mai azumi nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki(shan ruwa), da kuma farin ciki lokacin haduwarsa da ubangijinshi. Warin/yamin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda ya azumci ramadana, yana mai imani, da kwadayin Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbanshi.[Bukhari da Muslim]
2- SALLAR TARAWIHI/KIYAMUL-LAILI.

Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda yayi tsayuwa a ramadana, yana mai kwadayin Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubanshi.[Bukhari da Muslim]

3- SADAKA
Manzon Allah s.a.w ya kasance yafi kowa sadaka a Ramadana da waninsa, manzon Allah kyautarsa tafi iskan dake kadawa yawa, domin tana game kowa da kowa. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana cewa; "Mafificiyar sadaka, itace wacce akayi a cikin Ramadana.

4- CIYAR DA ABINCI

Akwai alkhairai kwarai da gaske a cikin ciyar da abinci, a Ramadana ne ko waninsa. Kamar yadda Allah s.w.t ya ambata siffofin mutanen kirki a cikin suratul insãn aya ta 8-12 saboda suna ciyar da abinci tare da zukatansu na cikin jin dadi da walwala lokacin da suke ciyarwar.
Magabata na kwarai sun kasance suna ciyar da abinci a ramadana kwarai da gaske, manzon Allah s.a.w yana cewa; "yã Ku mutane Ku watsa sallama, Ku ciyar da abinci, Ku sadar da zumunta, kutashi lokacin da mutane ke barci domin kuyi sallah, zaku shiga aljanna da aminci.[imamu Ahmad ya ruwaito da tirmidhi, Albany ya ingantashi].
Manzon Allah s. a.w yace: "Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da anrage mashi komai ba.[imamu Ahmad ya fitar, da nasa'i, Albany ya ingantashi.

5- NEMAN LAILATUL-KADRI.
Allah madaukakin sarki yana cewa: "Lallai mu muka saukar dashi (Qur'ani) a daren daraja, wa ya sanar dakai me ake cewa daren daraja, daren daraja yafi Alkhairi fiye da wata dubu.
Manzon Allah s. a.w yace; "Duk Wanda yayi tsayuwar daren lailatul-kadri, yana mai imani da kwadayin Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.[Bukhari da Muslim]

Lailatul-kadari ana nemanta a daren 21,23,25,27 ko 29. Hadisi ya tabbata daga  ummuna Aisha R.A tacewa manzon Allah s.a.w idan na dace da daren lailatul-kadari me zan fada? Sai yace mata kice; اللهم إنك عفو،تحب العفو،فعف أني
Ma'ana; "yã Allah kai mai yafiya ne, kanason masu yafiya, ka yafe mani.[Ahmad ya ruwaito da tirmidhi, Albany ya ingantashi].

6- YAWAITA ZIKIRI DA ADDU'AH DA ISTIGFARI.

Ya yan uwa
  Kwanakin watan ramadana masu tsada ne, mu daure mu ribacesu da yawaita zikiri da addu'ah, musamman a kebantattun lokuta na amsar addu'ah. Daga cikin lokuttan akwai;
* Lokacin da mai azumi zaiyi buda baki, ba'a maida addu'ah a wannan lokacin.

*  Daya bisa ukun dare, lokacin da Allah s.w.t yake saukowa yana cewa: "ina mai rokona in amsa mashi, ina mai neman gafara in gafarta mashi.

Daga karshe ina kwadaitar damu akan mu tsaya mu ribaci wannan wata mai albarka kafin ya wuce! Idan ya wuce bamu da tabbacin zamu kara riskarshi.

Allah ya tabbatar damu akan aikata abubuwan da suka dace da sunnah a cikin wannan wata mai albarka.

        WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.



COPYRIGHT©
Hashim ibn Surajo ibn Uba(ABU SINÃN)
ATS~TSAMAWY```

atstsamawy@gmail.com

http://hashimtsamiya.mywapblog.com

http://abbansinaan.mywapblog.com

http://abbansinan.WordPress.com

http://shababusunnahtsafe.mywapblog.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

https://free.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

+2348064734911
+2349030201868

Wednesday, 19 April 2017

AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH KO BIDI'AH???

🌺🍇🍏🌹🌷🌼🌸💐🌺
*AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???*
🌺💐🌸🌼🍇🌷🌹🍏🌺

(001)

Rubutawa: *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

بسم الله الرحمن الر حيم

```Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya chanchanci a bauta masa shi kadai kuma ya hanemu da shirkah, Tsira da Aminci su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w wanda ya tsoratar damu daga aikata bidi'ah.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda ganin ya dace mu fadakar da yan uwa musamman iyaye da kakanni da ake zalunta da hadissan karya, dangane da falalar watan Rajab.

Da farko dai shi watan Rajab yana daya daga watanni masu alfarma wanda aya ta 36a suratu taubah tayi bayani.

✏✏✏✏✏✏✏✏
MAGANGANUN MAGABATA AKAN AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI)
✏✏✏✏✏✏✏✏

kai tsaye yanzu ga Wata tambaya da akayi ma sheikh bin baaz(R.H) dangane da azumin Rajab(azumin tsofaffi).

An tambayi sheikh bin baaz(R.H) akan cewa shin ko yana halatta azumtar watan Rajab (AZUMIN TSOFAFFI) gaba dayansa? Domin wasu Malamai suna fadar cewa: duk wanda ya azumci Rajab, an gafarta mashi zunubbansa koda sun kai yawan kumfar teku, wasu kuma malaman sunyi hani da azumtar watan suna cewa; duk da zamanshi cikin watanni masu alfarma baya halatta a azumceshi baki daya???

Ga amsar da bin baaz ya bada, yana cewa; " Abun sani kawai shine ba'a shar'anta azumtar watan Rajab ba! Bari ma an karhantashi, abunda ya tabbata shine an shar'anta azumin sha'aban, manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumin sha'aban, yana azumyar sha'aban sai kadan yake  ragewa, amma Rajab an karhanta yin azumi a cikinsa, azumi a cikinsa yana daga cikin aikin jahiliyya, saboda masu azumtar basu da dalilin azumtar watan!!! Hadisan da ake yawo dasu akan falalar watan Rajab basu da asali, bari ma na karya ne wadanda basu inganta ba, abunda shari'ah ta shar'anta ga musulmai shine suci susha a watan Rajab, sai dai idan ya kasance kana yin azumin nafila tun kafin zuwan watan wanda su dama shari'ah ta tabbatar dasu, kamar; litinin da Alhamis, Ayyamul-beedh da sauransu, wannan yana da kyau kuma babu laifi, amma azumtar watan gaba dayansa, ko kuma baka saba yin azumin nafila ba sai da watan ya shigo sai ka fake da azumin nafila ka gabatar da na Rajab wannan shari'ah bata yadda dashi ba.
Wannan itace amsar da sheikh bin Baaz ya bada dangane da azumin tsofaffi na Rajab.

Hadisi ya tabbata daga Aisha matar Annabi Muhammad s.a.w tana cewa:كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يصوم حتى نقول لايفطر، ويفطر حتى نقول لايصوم، وما رأيته أكثر صياما منه في شعبان.
[صحيح أخرجه البحاري(١٩٦٩)، و مسلم(١١٥٦)].

Ma'ana; Aisha R.A take cewa; "Manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumi har sai nace bai cin abinci! Yana cin abinci har sai nace bai yin azumi(ma'ana yana yin azumi da yawa, haka kuma yana aje azumi ya huta sosai) ban taba ganin Manzon Allah s.a.w yana cika azumin wata daya ba sai dai idan ramadhan ne, ban taba ganin watan da yafi azumi a cikinsa ba face sha'aban.
[Bukhari da Muslim].

ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ " ‏( 25/290 ‏) :
" ﻭﺃﻣﺎ ﺻﻮﻡ ﺭﺟﺐ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ﻓﺄﺣﺎﺩﻳﺜﻪ ﻛﻠﻬﺎ
ﺿﻌﻴﻔﺔ ، ﺑﻞ ﻣﻮﺿﻮﻋﺔ ، ﻻ ﻳﻌﺘﻤﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻋﻠﻰ
ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻬﺎ ، ﻭﻟﻴﺴﺖ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﺮﻭﻯ ﻓﻲ
ﺍﻟﻔﻀﺎﺋﻞ ، ﺑﻞ ﻋﺎﻣﺘﻬﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﺿﻮﻋﺎﺕ ﺍﻟﻤﻜﺬﻭﺑﺎﺕ...

Shaikhul Islam Ibn taimiyyah (RH) y
ace: “Kebance watan rajab da yin azumi,
dukkan hadisan
da su ka zo akan haka da’ifai ne (masu
rauni), bari
ma hadisan karya ne, masu ilimi
basu amfani dasu, domin basu
cikin hadisan
da ake amfani dasu don nuna falalar
aikata abu,  bari ma dukkan su ma
hadisai ne
na karya..”
Duba Majmu’u Fatawa (25/290).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :
" ﻛﻞ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻲ ﺫﻛﺮ ﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻭﺻﻼﺓ ﺑﻌﺾ
ﺍﻟﻠﻴﺎﻟﻲ ﻓﻴﻪ ﻓﻬﻮ ﻛﺬﺏ ﻣﻔﺘﺮﻯ " ﺍﻧﺘﻬﻰ ﻣﻦ " ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ
ﺍﻟﻤﻨﻴﻒ " ‏(ﺹ 96 ‏)

Imam Ibnul Qaiyim (RH) y ace;
“Dukkan hadisan
da suka ambaci azumin watan rajab da
sallatar wasu
darare a cikin sa, hadisai ne na karya kuma
kirkirarru”.
Duba Almanarul Muniif (shafi 96).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺤﺎﻓﻆ ﺍﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﻓﻲ " ﺗﺒﻴﻴﻦ
ﺍﻟﻌﺠﺐ " ‏(ﺹ 11 ‏) :
" ﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ ﻓﻀﻞ ﺷﻬﺮ ﺭﺟﺐ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﺻﻴﺎﻣﻪ
ﻭﻻ ﺻﻴﺎﻡ ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻪ ﻣﻌﻴﻦ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺔ
ﻣﺨﺼﻮﺻﺔ ﻓﻴﻪ ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ﻳﺼﻠﺢ ﻟﻠﺤﺠﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ.

Alhafiz Ibn Hajar Al-Asqalani yake
cewa; “Babu
wani abu da aka ruwaito na falalar
watan Rajab,
ko yin azumi a cikin sa, ko azumtar
wasu adadin
kwanaki ayyanannu, ko tsayuwar
wasu darare
kebantattu”.
Duba Tabyinul Ajab (shafi 11).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺳﻴﺪ ﺳﺎﺑﻖ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ " ﻓﻘﻪ
ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 1/383 ‏) :
" ﻭﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻟﻴﺲ ﻟﻪ ﻓﻀﻞ ﺯﺍﺋﺪ ﻋﻠﻰ ﻏﻴﺮﻩ ﻣﻦ
ﺍﻟﺸﻬﻮﺭ , ﺇﻻ ﺃﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻷﺷﻬﺮ ﺍﻟﺤﺮﻡ , ﻭﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ
ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺃﻥ ﻟﻠﺼﻴﺎﻡ ﻓﻀﻴﻠﺔ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ,
ﻭﺃﻥ ﻣﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻤﺎ ﻻ ﻳﻨﺘﻬﺾ ﻟﻼﺣﺘﺠﺎﺝ ﺑﻪ
" ﺍﻧﺘﻬﻰ

Imam Sayyid Sabiq (RA) yake cewa;
“Azumin
watan rajab bashi da wani fifiko na
falala akan
waninsa cikin watanni, sai dai shi
yana daga cikin
watanni (guda hudu) ma su alfarma,
kuma ba a
samu a cikin sunnah ingatacciya ba cewa
yin azumi a
cikin sa yana da falala kebantacciya,
abunda ya zo
akan haka (ma’ana hadisan da suka
zo) ba a kafa
hujja dasu (domin da’ifai ne)”
Duba Fiqhus-Sunnah (1/383).

ﻭﺳﺌﻞ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻦ ﺻﻴﺎﻡ
ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﻭﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺘﻪ .
ﻓﺄﺟﺎﺏ :
" ﺻﻴﺎﻡ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ
ﻟﻴﻠﺘﻪ ﻭﺗﺨﺼﻴﺺ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺔ , ﻭﻛﻞ ﺑﺪﻋﺔ ﺿﻼﻟﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ " ‏( 20/440 ‏)

An tambayi sheikh Muhammad Salihul Usaimeen
(RH)
dangane da azumi ranar 27 ga watan
rajab da
kuma tsayuwar dararen sa.
Sai ya amsa da cewa:
“Yin azumi ranar 27 ga watan Rajab
da tsayuwar
darensa kebance shi da haka bidi’a
ne, dukkan
bidi’a kuma batace”
Duba Majmu’u fatawa na Usaimeen
(20/440).

   Haka zalika Sayyidina umar R.A ya kasance yana bulala akan wadanda ke kamewa akan azumin Rajab, yana ce musu kuci abinci, wannan watane da ya kasance ake girmamawa a lokacin jahiliyya. [Ibn Abi shaibah ya fitar 3/102] da ibn kathir a cikin musnadil- faruk 1/285]

Haka zalika ibn umar R.A ya kasance idan yaga mutane suna wuce gona da iri akan Rajab, yana kyamar hakan!
[Sahih: ibn abi shaibah ya fitar 3/102]

Ibn Abbas ya kasance yana hani akan azumin Rajab gaba dayansa, saboda kada a maida shi ya zama abunda za'a rinka yi duk shekara, wato a maidashi ya zama idi.
[Sahih; Abdulrazak ya fitar 7854].

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISAN DA SUKA INGANTA AKAN WATAN RAJAB!
✏✏✏✏✏✏✏✏
=  "kuyi axumi a cikinshi kuma kuci abinci a cikinshi.
[Sahih irwa'ul galeel 958]

= Sha'aban yana tsakanin Rajab da Ramadhan, ana shagaltar da mutane akanshi(domin samun saukin Ramadan) a cikin sha'aban ake daukar ayukkan bayi, ina kwadayin/inason kada a daga ayyukana face ina azumi.
[Isnadinsa mai kyau ne, silsilatus-sahiha 1898]

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISSAI DA'IFAI WADANDA MASU AZUMIN RAJAB KE KAFA HUJJA DASU.!!!
✏✏✏✏✏✏✏✏

= A cikin Aljanna akwai wani gulbi, ana kiransa Rajab, ruwansa suna da fari wanda farin yafi na nono, duk wanda yayi azumin Rajab na rana daya, Allah zai shayar dashi daga wannan gulbin.[Silsilatu-dha'ifah 1898]

= Rajab watan Allah, Sha'aban wata na(manzon Allah), Ramadan watan Al'umma ta.
Da'ifi ne, silsilatu-dha'ifah 4400]

= Darare guda biyar ba'a maida Addu'ah: 1. Farkon Daren Rajab. 2. Daren Rabin watan sha'aban. 3. Daren jumu'ah.  4. Daren karamar sallah. 5. Daren babbar sallah.
[Maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 1452]

= Rajab watane mai girma, Allah na lunka lada idan kayi aikin Alkhairi a cikinsa, duk wanda yayi azumin Rajab na kwana daya,kamar yayi azumin shekara. Duk wanda yayi na kwana bakwai, za'a rufe mashi kofofin wutar jahannama bakwai. wanda yayi na kwana takwas, za'a bude mashi kofofin Aljanna takwas. Wanda yayi na kwana sha biyar, mai kira zaiyi kira a sama yace; an gafarta maka abunda ya gabata na laifuka...[maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 5413]

✏✏✏✏✏✏✏✏
RUBABBUN HADISSAN DA YAN SHI'AH KE KAFA HUJJA DASU AKAN FALALAR WATAN RAJAB.
✏✏✏✏✏✏✏✏
Daga Baban hassan (A.S) yace; Annabi Nuhu (A.S) ya tuka jirgin ruwa a farkon watan Rajab, sai ya umurci wadanda ke tare dashi da su azumci wannan ranar, yace; "duk wanda ya azumci wannan ranar Allah zai nisanta shi da wuta na tsawon tafiyar shekara daya.

=Daga Abi Ja'afar, Muhammad ibn Aliyu(A.S) yace; duk wanda yayi azumi a Rajab na rana daya, a farkon Rajab ko tsakiyarsa ko karshensa, Allah ya wajabta mashi shiga Aljanna, kuma Allah zai sanya shi a tare damu a cikin darajojinmu na Ahlul baiti a ranar kiyama, wanda yayi na kwana biyu, Allah zai gafarta mashi duk zunubbanshi da suka gabata, wanda yayi na kwana uku, Allah zai gafarta mashi abunda ya gabatar na zunubi da wanda zaiyi a gaba sannan za'a bashi damar ceton yan uwanshi ma'abota zunubi...

= As-sadik Ja'afar  ibn Muhammad yace; "kada ka bari ranar ashirin da bakwai ga Rajab ta wuce ba tare da ka azumceta ba! Domin a ranar ne aka saukar wa Annabi Muhammad s.a.w Annabta...

Duka wadannan zaka samesu a cikin littafi mai suna FALALAR WATANNI UKU, wanda gingimemen malamin Shi'ah mai suna MUHAMMAD IBN ALIYU IBN HUSSAIN IBN MUSA AL-QUMMY ya rubuta.
Allah ka la'anci qummy.

  A takaice wadannan sune hujjoji na dangane da rashin ingancin azumin Rajab(azumin tsofaffi), duk wanda yake ganin akwai Gyara matukar gyaran nashi ya inganta hadisi ne ko aya ina maraba dashi kwarai da gaske.

Allah ya hadamu dani daku da sauran musulmai a cikin Aljannah.

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH...```


Copyright©
Dalibinku
*_Hashim Suraj Uba Tsamiya {ABU SINÃN}_*
☎08064734911
📞09030201868

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

17-07-1438AH
15-04-2017AC

Wednesday, 5 April 2017

MEETING

*MEETING! MEETING!! MEETING!!!*

```Kwamitin matasa na SHABABU AHLIS-SUNNAH WALJAMA'AH TSAFE, a karkashin jagorancin shugaban kwamitin ABDULHADI ADAMU SABO TSAFE, da Mataimakinsa HASAN GARBA TSAFE da sakataren kwamitin SULAIMAN LABARAN TSAFE, suna farin cikin gayyatar general meeting exco da members, domin tattauna muhimman Abubuwa.
Meeting din zai gudana kamar haka;

Wuri; Masjid mu'assasatu uthman bin Affan Tsafe.

Rana: Alhamis 06/04/2017

Lokaci: 08:00pm to 09:00pm( Please no Nigerian time!!!)

Allah ya bada ikon halarta akan lokaci.

Sanarwa: Daga ofishin jami'in huld'a da jama'ah (P.R.O)
Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINÃN)```

لا إله إلا الله

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*BAYANIN MA'ANAR LAA'ILAHA IL-LALLAHU!!!*
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺

*_001_*

_Rubutawa:_ *Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)*

*بسم الله الرحمن الر حيم*

*الحمد لله رب العالمين، وصلى الله وسلم وبارك على نبينا محمد وعلى آله وصحبه أجمعين.*

```Da farko ya kamata musan cewa ita wannan Kalmar itace ke rabewa tsakanin musulmi da wanda ba musulmi ba!
Wannan Kalmar akan ta aka aiko dukkan Annabawa!
Itace Kalmar dake tabbatar da tsoron Allah na hakika!
Itace igiyar nan mai karfi, wacce duk Wanda ya riketa zata kaishi Aljanna!

Abin lura: Wannan Kalmar ba fadarta a baki ko da halshe tare da jahiltar ma'anarta ke sanya musuluncinka ya inganta ba!

Domin kuwa munafukai suna fadarta a bakunansu, amma kuma Allah yace" suna chan kasan wuta" a suratun nisa'i aya ta 145, tare da cewa suna Sallah suna sadaka, watakila har wurin wa'azi suna halarta.

Abunda ya kamata ga duk wanda ya fadeta, toh ya san ma'anarta har a zuciya ya kudurceta(ma'anarta, sharuddanta, falalarta, da abunda ta kunsa na tauhidi da akeeda) dole ne kaso Kalmar, kaso mai son Kalmar, dole ne ka yaki duk mai adawa da Kalmar ko mai saba mata.

Ita Kalmar LAA'ILAHA- IL-LALLAH! korewa ne da kuma tabbatarwa. Kore ilahantaka ga duk wani wanda ba Allah ba! Koda kuwa Manzo ne, ko Annabi, ko Mala'ika, ko wani mutumin kirki, ko gausi ko waliyyi koma Waye!  Tare da tabbatar da ilahantaka ga Allah shi kadai.

Na daga cikin mas'alolin jahiliyya wanda Annabi Muhammad s.a.w ya saba musu; Bautar mutanen kwarai ta Hanyar Neman biyan bukatunsu da nufin su nema musu ceto a wurin Allah, saboda zatonsu akan cewa Allah na son hakan. Kamar yadda Allah s.w.t yake cewa;
*ويعبدون من دون الله ما لا يضرهم ولا ينفعهم ويقولون هؤلاء شفعؤنا عند الله.* {يونس ١٨}

Ma'ana: "Suna bautar wani wanda ba Allah ba, Wanda bai iya cutar dasu, kuma bai iya amfanar dasu, har ma zakuji suna fada cewa wadancan sune masu cetonmu a wurin Allah"

Wannan ayar in muka lura zatayi aiki ga masu Dariku da yan shi'ah! Saboda suma zakuji suna fadar irin wadannan kalmomin, bari ma, wani lokaci nasu sunfi muni da hadari.

Muna rokon Allah s.w.t ya tabbatar damu akan tauhidi da akeeda Allah ka kara mana Ikhlasi.

Wannan mukaddima ce, amma bayanin zaizo a fitowa ta gaba insha Allahu.

Copyright©
Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)
08064734911```

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

Thursday, 30 March 2017

QARYA ADO A WAJEN YAN SHI'AH

*'KARYA ADDININ YAN SHI'AH!!!*
**

**

**
```Don haka ne ibn Taimiyya a cikin minhajis-sunnah 1/59 yake cewa; Malamai ma'abota ilimi sunyi ittafaki(sun hadu) akan hakaitowa da ruwayoyi da isnadi akan cewa yan Shi'ah(Rafidhawa) makaryata ne na gaske, kuma karya a wajensu dadadden abune ba wai yau suka fara ba.
Haka shima ABU HATIM-ARRAZY yake cewa naji yunus ibn Abdul-a'ala yana cewa; Ash-hab ibn Abdul-aziz  yace: An tambayi IMAMU MALIK akan yan shi'ah? Sai IMAMU MALIK yace; kada kuyi magana dasu! Kada Ku  ruwaito magana ko wani Abu da zai amfani Al'umma daga garesu! Domin su makaryata ne.

Wannan kuwa kowa na iya gasgata hakan a wannan zamani da muke ciki

((YAA KU WADANDA SUKAYI IMANI, KU KARE KAWUNANKU DA IYALANKU DAGA WUTA! WACCE MAKAMASHINTA MUTANE DA DUWATSU))

Allah ka  kare musulmai daga makirci da sharrin yan Shi'ah a duk inda suke```

Copyright©
*Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINÃN)*
📞08064734911☎

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

Monday, 13 March 2017

MUNA NEMAN ADDU'AH

KWAMITIN  Shababu Ahlus Sunnah Waljama'ah TSAFE, wadannan matasa da kuke gani yanzu haka dukkaninsu suna matakin karatu na jami'ah, kuma yanzu haka suna fuskantar exams, da wannan ne  kwamitin keson Ku taimaka Ku sanya su cikin addu'oinku na yau da kullum domin samun nasarar wannan jarabawa.

Daga; kwamitin  matasa na Shababu Ahlissunnah waljama'ah tsafe.